Posts

Showing posts from April, 2022

Eid El-Fitr: Anga jinjirin watan Shawwal a Nijar

Image
Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta sanar da cewa za a yi bikin ƙaramar Sallah a gobe Lahadi, bayan ganin jinjirin watan Shawwal a sassan ƙasar.

Eid-el-Fitr: Hukumar SEMA ta tallafawa ‘yan gudun hijira

Image
Eid-el-Fitr: Hukumar SEMA ta tallafawa ‘yan gudun hijira    Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA) Hajiya Yabawa Kolo ta rabawa ƴan gudun hijira kayan abinci Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA) Hajiya Yabawa Kolo ta ƙaddamar da rabon kayan abinci ga ‘yan gudun hijira a sansanin Gubio da ke wajen birnin Maiduguri, gabanin bikin ƙaramar Sallah da ke tafe. Da take jawabi yayin rabon kayan abinci a ranar Asabar, Yabawa Kolo ta ce kayan da hukumar ta rabawa ƴan hijirar gudumuwa ce da Gwamna Babagana Zulum ya bada umarnin a rabawa marasa galihu. Ta kuma jaddada cewa sansanin ‘yan gudun hijira na Gubio yana daya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira mafi girma a halin yanzu a cikin birnin Maiduguri da ke da ‘yan gudun hijira sama da dubu 10,000 biyo bayan rufe wasu sansanonin ‘yan gudun hijira da gwamnatin jihar Borno ta yi tare da sake tsugunar da ‘ya hijirar ta hanyar da ta...

Sarkin Musulmi Ya Bada Umarnin Duba Watan Karamar Sallah

Image
Sarkin Musulmi Ya Bada Umarnin Duba Watan Karamar Sallah Daga Ibrahim Ammani Fadar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ta fitar da wata sanarwar da ke ƙira ga Musulman Najeriya su fara neman sabon watan Shawwal daga yau Asabar. Sanarwar wadda Arc. Zubairu Haruna Usman-Ugwu – wanda shi ne shugaban gudanarwa na hukumar NSCIA – ya sanya wa hannu, ta ce “Kwamitin Ganin Wata na ƙasa (NMSC), Sarkin Musulmi ya umarci al’ummah Musulmi a Najeriya su fara duba sabon watan Shawwal daga Asabar 30 ga watan Afrilu 2022, wanda yayi daidai da 29 ga watan Ramadan, 1443 AH. Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Idan Musulmai masu daraja suka ga jinjirin watan, sai Mai Alfarma Sarkin Musulmi zai sanar da ranar Lahadi 1 ga watan Mayun 2022 a matsayin ranar 1 ga watan Shawwal kuma ranar eid-fitr kenan. Amma, idan ba a ga jinjirin watan ba a wannan ranar, ranar Litinin 2 ga watan Mayun 2022 ta zama ranar Idul Fitr ke nan. A ƙarshe sanarwar ta ce ana iya tuntuɓar dukkan jagororin al’umma a dukkan sassa...

Fashewar bama-bamai ya sanya firgici a zuƙatan mazauna birnin Maiduguri.

Image
Ƙarar fashewar wasu abubuwa da ake kyautata zaton cewa bama-bamai ne sun sanya firgici a zuƙatan mazauna birnin Maiduguri. Daga Yasir Sabo, Maiduguri Kafar jaridar YERWA EXPRESS ta ruwaito cewa majiyoyin tsaro masu sahihanci sun shaida mata cewa ƙarar fashewar daga ɓangaren jami'an tsaro soji ne suna tauna tsakua ne domin aya taji tsoro. Wani jami’in Sa kai na ƙungiyar Civilian JTF ya shaidawa Yerwa Expresd cewa "a daren nan an ga shawagin ‘yan Boko Haram/ISWAP a kusa da garin Kayamla shi yasa jami'an tsaron suka yi shirin ko ta kwana. Yace a halin yanzu 'yan ta'addan sun yi ƙone-ƙone a ƙauyen na Kayamla don haka sojoji suka yi shiri tsab "kuma wannan Fashe-fashen da kuke ji daga sojojinmu ne domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma" inji majiyar.

EID-EL-FITR: POLICE IN BORNO COMMIT TO PROTECT LIVES, PROPERTY

Image
EID-EL-FITR: POLICE IN BORNO COMMIT TO PROTECT LIVES, PROPERTY   By  Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri Borno State Police Command reitetates its commitment to protect lives and properties during and after Eid-El-Fitr Festivities. The state Police Public Relation Officer PPRO ASP Sani Kamilu Muhammad Shatambaya stated this in an interview in his office in Maiduguri. This comes after terrorists threatened to detonate bombs in Maiduguri, Bama and Konduga local government areas during sallah celebration. The Police Command reiterated its redness to provide adequate security for lives and property before, during and after the forthcoming Eid-El-Fitr celebration and assures  of sufficient deployment of Police personnel to EID praying grounds, and other public places across the state to ensure the safety of residents during the celebration and beyond. The Police Public Relations Officer said the Command will not hesitate to clamp down on any miscreant who may want to use...

DSS Ta Bankaɗo Shirin Tayar Da Bama-Bamai Lokutan Bikin Sallah

Image
Daga Ibrahim Ammani Rahotannin daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Hukumar ‘Yan Sandan farin kaya ta DSS ta bayyana gano shirin kai hari akan wuraren ibada da wuraren shakatawa da kuma wasu kadarorin gwamnati musamman lokacin bikin Sallah da bayan sa. Mai Magana da yawun Hukumar Peter Afunanya ya bayyana haka a sanarwar da ya rabawa manema labarai, inda yake zargin mutanen cewar suna shirin mayar da kasar irin halin da ta samu kanta kafin shekarar 2015 inda ake samun fashe fashen makamai. Jami’in ya bukaci jama’a da su zuba ido domin lura da abubuwan da suke faruwa a yankunan su, yayin da suke gudanar da harkokin su na yau da kullum, tare da gabatarwa jami’an tsaro da bayanan duk wani abinda basu gamsu da shi ba a yankunan su.

Mutuwar Oyo Adeyemi Babban Rashi Ne Ga Najeriya- Buhari

Image
Mutuwar Oyo Adeyemi Babban Rashi Ne Ga Najeriya- Buhari            Daga Ibrahim Ammani Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jajanta wa gwamnatin Jihar Oyo da al’ummar jihar sakamakon rasuwar sarkin Yarabawa madi girma Alafin na Oyo, Lamidi Olayiwola Adeyemi III, ranar Juma’a. A ranar Asabar aka yi jana’izar sarkin a tsohon garin Oyo, inda aka binne shi a farfajiyar masarautarsa. Marigayin ya rasu yana da shekaru 83 a wani asibiti da ke jihar Ekiti bayan ya yi fama da jinya.

Da Ɗumi-Ɗumi: Sarkin Oyo mai mata barkatai, Oba Lamidi, ya rasu

Da Ɗumi-Ɗumi: Sarkin Oyo mai mata barkatai, Oba Lamidi, ya rasu  Rahotanni daga jihar Oyo na nuni da cewa Allah ya yiwa Sarkin Oyo rasuwa. Basarake mafi girma a ƙasar Yarbawa, Oba Lamidi Adeyemi ya rasu da yammacin ranar Juma'a a Asibitin koyarwa na jami'ar Afe Babalola dake Ado Ekiti.  Tsadar daren ranar Juma'a ne aka gaggauta kai gawarsa jihar Oyo domin fara shirin jana'izarsa. Marigayi Adeyemi ya rasu yana da shekaru 83 bayan kwashe shekaru 52 kan mulki. 

Zaɓen 2023: ƙungiyoyi 150 sun ɓuƙaci Zulum tsayawa takara karo na biyu.

Image
  Zaɓen 2023: ƙungiyoyi 150 sun ɓuƙacu Zulum ya tsayawa takara karo na biyu. Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri Zaɓen 2023: Ƙungiyoyi a birnin Maiduguri 150 sun tsaida aniyar tarawa Zulum miliyan 50 don takarar gwamna ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC. Umar Shettima mai magana da yawun ƙungiyoyin. Jaridar Magarya ya bayar da rahoton cewa, gamayyar ƙungiyoyin da suka fito da wannan matsayar sun bayyana aniyar su ne ranar Juma'a yayin taron manema labarai da suka gudanar a sakatariyar ƙungiyar ƴan jaridu da ke birnin Maiduguri.  Mai magana da yawun ƙungiyar Umar Shettima, ya ce ƙungiyoyin suna da muradin gwamna Babagana Umara Zulum ya ci gaba da zama a kan karagar mulki bisa la’akari da irin ayyukan da ya yi a wa’adinsa na farko.  Sannan yace ƙungiyoyin sun ƙunshi ƙwararrun malamai, ma'aikatan kiwon lafiya, sufuri da ƙungiyoyin mata da dai sauransu.  Hakazalika sun buƙaci al’ummar jihar Borno da su mara musu goyon bayansu ta hanyar bayar da gu...
  Zaɓen 2023: ƙungiyoyi 150 sun ɓuƙaci gwamna Zulum ya tsaya takara karo na biyu. Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri Zaɓen 2023: Ƙungiyoyi a birnin Maiduguri 150 sun tsaida aniyar tarawa Zulum miliyan 50 don takarar gwamna ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC.  Jaridar Magarya ya bayar da rahoton cewa, gamayyar ƙungiyoyin da suka fito da wannan matsayar sun bayyana aniyar su ne ranar Juma'a yayin taron manema labarai da suka gudanar a sakatariyar ƙungiyar ƴan jaridu da ke birnin Maiduguri.  Mai magana da yawun ƙungiyar Umar Shettima, ya ce ƙungiyoyin suna da muradin gwamna Babagana Umara Zulum ya ci gaba da zama a kan karagar mulki bisa la’akari da irin ayyukan da ya yi a wa’adinsa na farko.  Sannan yace ƙungiyoyin sun ƙunshi ƙwararrun malamai, ma'aikatan kiwon lafiya, sufuri da ƙungiyoyin mata da dai sauransu.  Hakazalika sun buƙaci al’ummar jihar Borno da su mara musu goyon bayansu ta hanyar bayar da gudumawar siyar fom domin ana buƙatar kudi yayin yaƙin neman ...