Manchester City Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila

Manchester City Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila

    Daga Jaridar Magarya

Gundogan da Jesus suna murnar jefa kwallo.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester City ta lashe kofin gasar Firimiyar Ingila ta bana bayan ta farke ƙwallaye biyu da Aston Villa ta zira mata a filin wasa na Etihad.

Wannan shi ne dai karo na shida da ƙungiyar ta lashe gasar a tarihi.

Ƙungiyar da Pep Guardiola ke jagoranta ta kare kakar ta bana da tazarar maki daya kacal tsakaninta da Liverpool, wadda ta doke Wolves 3-1 a wasan ƙarshen da aka fafata a Yammacin ranar Lahadi.

Ƙwallo biyu da Ikay Gundogan ya ci da kuma wadda Rodri ya zira a cikin minti shida kacal su ne suka bai wa City nasara inda ta lashe wasan da 3-2.

Villa ta shiga gaba a wasan tun farko ta hannun Matty Cash da Philippe Coutinho.

Comments

Popular posts from this blog

In Maiduguri, a 15-year-old girl was killed by a stray bullet from CJTF

The hospital has discharged minors who were victims of viral child abuse videos and they are currently recovering well.

BORNO: In Benishiekh, a man was killed during a tragic dispute over mango farming