Borno: Boko Haram Sun Kai Hari A Ƙauyen Kautikari

 Borno: Boko Haram Sun Kai Hari A Kautikari


Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri


Rahotanni daga ƙauyen Kautikari na ƙaramar hukumar Chibok dake kudancin jihar Borno na cewa wasu da ake kyautata zaton mayaƙan Boko Haram ne sun kai haei da maraicin nan.


Da yake jawabi ga wakilinmu na jihar Borno DPO na Ƴan sandan ƙaramar  hukumar Chibok ya tabbatar da faruwar lamarin. Inda yace "Dazu da yamma na samu labarin wasu mahara sun kai hari garin Kautikari kuma tuni jami'an ƴan sanda suka kai ɗaukin gaggawa sai dai har zuwa yanzun bamu san halin da ake ciki ba" Muna sa ran da safe zamu samu damar yin ƙarin kan abin da ya faru" inji shi.

Comments

Popular posts from this blog

In Maiduguri, a 15-year-old girl was killed by a stray bullet from CJTF

The hospital has discharged minors who were victims of viral child abuse videos and they are currently recovering well.

BORNO: In Benishiekh, a man was killed during a tragic dispute over mango farming